DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta zabi Idahosa a matsayin mataimakin gwamnan Edo a zaben da yake gabatowa

-

 APC ta zabi Idahosa a matsayin mataimakin gwamnan Edo a zaben da yake gabatowa.

Google search engine

Jam’iyyar (APC) ta tsayar da Hon. Dennis Idahosa a matsayin mataimakin dan takarar gwamna a zaben gwamnan Edo da za a yi ranar 21 ga watan Satumbar shekarar da muke ciki.

Shugaban jam’iyyar APCn na kasa, Abdullahi Umar Ganduje da sakataren jam’iyyar na kasa, Sen. Ajibola Bashiru za su gabatar da Sanata Monday Okpebolo, a matsayin dan takarar gwamnan da kuma abokin takararsa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a villa dake Abuja.

Idahosa shine ya maye gurbin Hon. Omoregie Ogbeide-Ihama wanda dan takarar gwamnan ya bayyana a makon da ya gabata a matsayin abokin takararsa.

Jaridar Nation ta rawaito cewa Idahosa, dan majalisar wakilai, an tabbatar dashi a daren ranar Lahadi bayan wani dogon zama da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar Edo, da shugabannin jam’iyyar da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima suka yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara