DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana hasashen cewa ambaliyar ruwa za ta shafi jihohin Nijeriya 31 a bana

-

 Ana hasashen cewa ambaliyar ruwa za ta shafi jihohin Nijeriya 31 a bana

Google search engine

Gwamnatin tarayya ta rubutawa gwamnoni 31 takardar sanar da su halin da ake ciki na ambaliyar ruwa a jihohinsu tsakanin watan Afrilu zuwa Nuwamba na wannan shekara ta 2024.

Ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli Farfesa Joseph Utsev ne ya bayyana hakan a ranar Talata a Abuja yayin da yake yi wa manema labarai karin haske kan hasashen ambaliyar ruwa na shekara ta 2024.

A wajen taron, hukumar kula da ayyukan ruwa ta Nijeriya, an bayyana cewa an ware kananan hukumomi 148 a jihohin Legas, Kano, Delta, da kuma wasu jihohi 28 a matsayin wuraren da ake fama da matsalar ambaliya.

Hasashen da aka samu na shekara ta 2024 na ambaliyar ruwa ya nuna cewa wani bangare na kananan hukumomi 148 a cikin jihohi 31 na tarayya sun fada cikin yankunan da ake fama da matsalar ambaliya, yayin da wani bangare na kananan hukumomi 249 da ke cikin jihohi 36 na tarayya da kuma babban birnin tarayya Abuja sun fada cikin tsaka mai wuya.

Jihohin da ke fama da matsalar ambaliya sun hada da Adamawa, Akwa-Ibom, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Kogi, Kwara, Legas , Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara