DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan kano ya nemi a gina makarantar soji ta mata a Kano.

-

Gwamna ya nemi a gina makarantar soji ta mata a Kano.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci a kafa makarantar sakandare ta ‘yan mata ta sojojin sama a Kano domin karawa akan makarantar sakandaren maza da ke Kwa, karamar hukumar Dawakin Tofa, a kan hanyar Kano zuwa Katsina.

Google search engine

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya fitar, Gwamna Abba ya yi wannan roko yayin ziyarar da shugaban hafsan sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Hassan Bala Abubakar ya kai gidan gwamnati a Kano.

Ya kuma nuna jin dadinsa a bisa kwarewa da kuma tarihin Air Marshal Abubakar, inda ya yaba da kokarin rundunar sojin saman kasar nan wajen magance kalubalen tsaro, musamman wajen yakar masu garkuwa da mutane, ‘yan fashi, da sauran masu aikata laifuka a Kano.

Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatinsa na tallafawa rundunar sojin sama da kuma ‘yan uwa jami’an tsaro, inda ya jaddada muhimmancin hadin kan su wajen wanzar da zaman lafiya a Kano da kasa baki daya.

 A nasa jawabin Air Vice Marsha Hassan Abubakar, ya nuna damuwarsa kan yadda ake ci gaba da yankad filin jirgin saman NAF da matsugunin sa, inda ya bukaci a maido da filin da aka sadaukar domin fadadawa nan gaba.

Ya kuma nemi goyon bayan Gwamna Abba wajen hada cibiyar samar da ruwan sha ta jihar Kano da na matsugunin sojojin sama domin inganta samar da ruwan sha a Jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara