DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bola Tinubu ya nada shugaban hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya sanar da nadin DIG Hashimu Argungu (Rtd) a matsayin shugaban hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda wato ‘Police Service Commission’.
Kazalika, shugaban kasar ya kuma amince da nadin Chief Onyemuche Nnamani a matsayin Sakataren hukumar da kuma DIG Taiwo Lukanu (Rtd) a matsayin mamba a hukumar.
Bugu da kari, shugaban kasar ya kuma amince da nadin Mohammed Seidu a matsayin shugaban asusun tallafa wa ‘yan sanda na ‘Police Trust Fund’.
Wadannan nade-nade na a cikin wata sanarwa daga mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai Mr Ajuri Ngelale da DCL Hausa ta samu kwafi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara