DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mazauna Kaduna, Kano da Katsina na fama da tashin farashin abinci a kasuwanni

-

Mazauna Kaduna, Kano da Katsina na fama da tashin farashin abinci a kasuwanni

Google search engine

Al’ummar Nijeriya na fuskantar hauhawar farashin kayayyakin abinci da ba a taba yin irinsa ba.

Binciken da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya fitar ya nuna cewa a jihohin Kaduna, Kano da Katsina, al’ummar jihohin na fama da hauhawar farashin kayayyakin abinci.

A wani bincike da NAN ya gudanar a jihohin ya nuna cewa ana samun karuwar farashin shinkafa, biredi, sikari, garri, nama da kwai da dai sauran su, wadanda su ne abubuwan da ake amfani da su a gidaje.

Hauhawar farashin ya yi tasirin gaske ga al’umomin da suke jihohin, wanda hakan ya sa wasu gidajen ba su iya cin abinci sau uku a rana kamar yadda aka saba.

Binciken ya gano cewa mazauna Kaduna,Katsina da kuma Kano na kokawa bisa yadda kayan abinci suke tashin gauron zabi inda suka bayyana cewa kullum kayan kara tashi suke yi ba tare da wani dalili ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara