DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC kan batun zanga-zanga

-

Tinubu ya shiga ganawar sirri da gwamnonin APC kan batun zanga-zanga 

Google search engine

Shugaba Bola Tinubu yana ganawa da gwamnonin jam’iyyar APC karkashin kungiyar gwamnonin Progressives Forum a fadar sa da ke Abuja.

Taron wanda aka fara da misalin karfe 1, ya biyo bayan kiraye-kirayen da ake yi na zanga-zangar adawa da matsalar tattalin arziki a fadin Nijeriya.

Ko da yake ba a san ajandar taron ba, amma ana iya danganta shi da zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a ranar 1 – 10 ga Agusta.

Zanga-zangar wacce aka shirya a karkashin taken ‘EndBadGovernance’ ta samu karbuwa sosai a shafukan sada zumunta duk da cewa wadanda suka shirya zanga-zangar ba a bayyana sunansu ba,kuma ba babu sunan wata kungiya da ta dauki nauyi a hukumance ba.

Wannan taron ya biyo bayan kammala taron kungiyar gwamnonin Nijeriya da aka yi a daren Larabar da ta gabata, kuma ya biyo bayan soke taron Majalisar Tattalin Arzikin kasa da aka shirya gudanarwa a yammacin ranar Alhamis dinnan.

Wadanda suka hallarci taron sun hada da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ministan kasafin kudi da tsare-tsare na tattalin arziki, Wale Edun da Abubakar Bagudu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara