Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnati baza ta lamunta da tashin hankali ba yayin zanga-zangar da ake shirin yi.
Gwamnan ya yi wannan kira ne yayin da yake jawabi ga yan kasuwa, sarakunan gargajiya, da malaman addini a gidan gwamnati da ke Kano a yau ranar Laraba.
Gwamnan dai ya jaddada cewa, zanga-zanga ba ta da wani alfanu . Yayi kira ga masu son yin amfani da yancinsu na yin zanga-zangar da su guji yin barna don kaucewa bata gari da za su yi amfani da su.




