DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu garkuwa da mutane sun nemi naira miliyan 300 na fansar karamin yaro da ‘yan uwansa da suka sace a Kaduna

-

Masu garkuwa da mutane da suka dauke yara 4 a jihar Kaduna sun tuntubi mahaifin yaran tare da neman naira miliyan 300 a matsayin kudin fansa.

Google search engine
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa sun yi barazanar kashe karamin yaron dan shekaru biyu saboda kukan da yake yi.
Mahaifin yaran wanda ke zaune a Keke A, karamar hukumar Chikun, ya ce lokacin da suka kira shi yana ji lokacin da suke dukan yaran, ba yadda zai yi.
Yan bindigar sun sace yaran ne a lokacin da mahaifinsu ya ce asibiti domin duba mahaifiyarsu wadda aka kwantar da ita saboda rashin lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara