DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An gurfanar da ‘yan kasar waje 113 akan laifukan yanar gizo da shigowa Nijeriya ba bisa ka’ida ba

-

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta ce ta gurfanar da wasu ‘yan kasar waje 113 da laifukan da suka shafi yanar gizo, wadanda suka hada da zamba da safarar kudade da dai sauran su. 
Wani bayani da mai magana da yawun rundunar ya wallafa a shafinsa na X, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ofishin rundunar ‘yan sanda mai yaki da laifukkan yanar gizo ne ya kama mutanen a ranar 3 ga watan Nuwamban 2023 a birnin tarayya Abuja.
Wadanda aka kama a yayin sammen, na fuskantar zarge-zarge ciki har da wadanda suka shafi shige da fice da kuma safarar bil adama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ministan yada labarai ya nesanta kansa da wani rubutu mai taken “Malagi 2027”

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a na Nijeriya, Mohammed Idris, ya nesanta kansa daga wani rubutu na siyasa mai taken “Malagi 2027”, wanda...

Wasu tsoffin ‘yan sanda sun roki Tinubu da ya sa a mayar da su aiki bayan tilasta yi musu ritaya

Wasu tsoffin jami’an rundunar ’yan sandan Nijeriya sun sake kira ga rundunar da ta bi hukuncin Kotun Kwadago ta Kasa, wadda ta bayar da umarnin...

Mafi Shahara