DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya tura sunayen mutane 5 zuwa ga majalisar dokokin jihar domin ta tantancesu a matsayin kwamishinoni.
Kakakin majalisar dokokin jihar Isma’il Jibrin Falgore ne ya karanta wasikar gwamnan a zaman majalisar na yau Litinin, a cewar jaridar Dailytrust.
Mutanen da gwamnan ke son majalisa ta tantance sun hada da tsohon shugaban ma’aikatan fadar gwamnatinsa, Shehu Sagagi, da Dr Dahiru Mohd Hashim, da Ibrahim Abdullahi Wayya, da Dr Isma’il Dan Maraya, da Gaddafi Sani Shehu da kuma Abdulkadir AbdulSalam.
Wannan na zuwa ne, kwanaki kadan bayan da gwamnan ya kori sakataren gwamnati Abdullahi Bichi, tare da wasu kwamishinoni 5 tare da roshe ofishin shugaban ma’aikata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wasu tsoffin ‘yan majalisar dokokin Kano sun yi mubaya’a ga Barau Jibrin a takarar gwamna a 2027

Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya Barau Jibrin baya don...

Gwamnati ta binciki ta’azzarar matsalar tsaro a Nijeriya – Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya ta da gudanar da bincike kan musabbabin ta'azzarar matsalar tsaro a wasu...

Mafi Shahara