DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya tura sunayen mutane 5 zuwa ga majalisar dokokin jihar domin ta tantancesu a matsayin kwamishinoni.
Kakakin majalisar dokokin jihar Isma’il Jibrin Falgore ne ya karanta wasikar gwamnan a zaman majalisar na yau Litinin, a cewar jaridar Dailytrust.
Mutanen da gwamnan ke son majalisa ta tantance sun hada da tsohon shugaban ma’aikatan fadar gwamnatinsa, Shehu Sagagi, da Dr Dahiru Mohd Hashim, da Ibrahim Abdullahi Wayya, da Dr Isma’il Dan Maraya, da Gaddafi Sani Shehu da kuma Abdulkadir AbdulSalam.
Wannan na zuwa ne, kwanaki kadan bayan da gwamnan ya kori sakataren gwamnati Abdullahi Bichi, tare da wasu kwamishinoni 5 tare da roshe ofishin shugaban ma’aikata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jihohin APC sun sake mara wa Tinubu baya matsayin dan takara a zaɓen 2027

Jam’iyyar APC a jihohi da dama ta sake bayyana goyon bayanta ga shugaba Bola Tinubu, a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben...

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Mafi Shahara