DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An shiga rudani a kotun da’ar ma’aikata ta Nijeriya kan rikicin shugabanci

-

Tambarin Kotun da’ar ma’aikata 

Har yanzu tsugune ba ta kare ba a kotun da’ar ma’aikata ta Nijeriya CCT yayin da ake takun-saka tsakanin shugabanta, Danladi Umar da sabon shugaban da aka nada, Mainasara Kogo, waɗanda ko wannensu ke ayyana kan sa a matsayin shugaba. 

Binciken da jaridar Dailytrust ta yi ya nuna cewa mutanen biyu ko wanne ya je ya tattaunawa da ma’aikatan kotun ba tare da wani kwakkwaran umarni kan wane ne shugaba ba. 

A ranar 13 ga watan Yuli ne shugaba Bola Tinubu ya nada Kogo a matsayin sabon shugaban kotun ta CCT, kazalika a wannan rana ce ya bayyana Omolola Oloworaran a matsayin Darakta Janar na Hukumar Fansho ta Kasa wato PENCOM. 

Su dai ma’aikatan sun koka kan yadda ake tafiyar da aikin kotun tun bayan da aka fara cece-ku-ce kan batun tsige Danladi Umar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Cin hanci la’ana ce, mu tsabtace kanmu daga rashawa- EFCC

A wani sakon tunatarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook albarkacin ranar Juma’a, hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya,...

Mafi Shahara