DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu, gwamnoni, shugabannin majalisa, da wasu jagorori sun yi kira da a rungumi zaman lafiya, da hadin kai a yayin bukukuwan Kirsimeti

-

Bola Ahmad Tinubu, Shugaban Nijeriya 

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu da gwamnonin kasar da shugabannin majalisa da wasu jagorori sun yi kira da a rungumi son juna, zaman lafiya da kuma hadin kai, a daidai lokacin da mabiya addinin kirista ke bukukuwan Kirsimeti a fadin duniya.
Shugabannin sun kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi addu’a ga masu mulkin kasar domin dorewar ci gaban kasar.
Daga cikin wadanda su ka yi wadannan kiraye-kirayen har da kakakin majalisar wakilai Abbas Tajuddeen, mataimakin shugaban majalisar dattawa Sanata Barau Jibril, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da kuma gwamnonin Kwara, Gombe, Bauchi da Nasarawa da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

SGF George Akume ya angwance da tsohuwar matar Ooni na Ife Gimbiya Zainab

Sakataren Gwamnatin Nijeriya (SGF), Sanata George Akume, ya auri Sarauniya Zaynab Ngohemba, tsohuwar matar Ooni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi.   Jaridar Punch ta ce an...

Jirgin yakin Nijeriya da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal

Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya ta tabbatar da cewa jirgin ta kirar C-130 mai lamba NAF 913 ya isa cibiyar gyara jirage ta OGMA da...

Mafi Shahara