DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu, gwamnoni, shugabannin majalisa, da wasu jagorori sun yi kira da a rungumi zaman lafiya, da hadin kai a yayin bukukuwan Kirsimeti

-

Bola Ahmad Tinubu, Shugaban Nijeriya 

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu da gwamnonin kasar da shugabannin majalisa da wasu jagorori sun yi kira da a rungumi son juna, zaman lafiya da kuma hadin kai, a daidai lokacin da mabiya addinin kirista ke bukukuwan Kirsimeti a fadin duniya.
Shugabannin sun kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi addu’a ga masu mulkin kasar domin dorewar ci gaban kasar.
Daga cikin wadanda su ka yi wadannan kiraye-kirayen har da kakakin majalisar wakilai Abbas Tajuddeen, mataimakin shugaban majalisar dattawa Sanata Barau Jibril, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da kuma gwamnonin Kwara, Gombe, Bauchi da Nasarawa da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kashi 8 cikin 100 na ‘yan Nijeriya ne kawai ke iya wanke hannu yadda ya kamata a cewar UNICEF

Asusun tallafawa kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya ce kaso 92 cikin 100 na 'yan Nijeriya ba sa iya wanke hannu yadda ya...

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin kasar CBN kan wasu cajin kudade da bankuna ke yi wa al’umma

Majalisar wakilan Nijeriya ta gayyaci Gwamnan babban bankin CBN, Olayemi Cardoso, tare da shugabannin manyan bankuna domin bayyana dalilin cajin kudade ba tare da daliliba...

Mafi Shahara