DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana zargin wata mata da yin ajalin mijinta ana shirye-shiryen bikin sunan ɗansa

-

 

‘Yan sanda

An kama wata mata mai suna Fatima Dzuma ‘yar kimanin shekaru 27 bisa zargin ta da ajalin mijinta Baba Aliyu mai shekaru 25 a jihar Neja.

Lamarin dai ya faru ne a kauyen Lafiyagi Dzwafu da ke karamar hukumar Katcha ta jihar, a lokacin da ake shirye shiryen bikin nadin sunan dansa da matarsa ta farko ta haifa masa.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, Abiodun Wasiu, ya ce an kama Fatima ne bayan an gano gawar mijinta a wani daji da ke kusa da gidansu, kwanaki uku bayan an nemeshi an rasa.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, kakakin ‘yan sandan ya ce wadda ake zargin ta amsa laifin da ake tuhumar ta da shi, inda ta ce a lokacin da mijin ta yake barci ta halaka shi, sannan ta daure shi da igiya kafin ta jefar da gawar a cikin daji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara