DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan gwagwarmaya Kemi Seba ya bayyana aniyar sa ta takarar shugaban kasa a Jamhuriyar Benin

-

 

Google search engine

Fitaccen dan gwagwarmayar nan mai fafitikar cigaban Afirka dan kasar Bénin Kemi Seba, ya bayyana aniyar sa a hukumance ta tsayawa takarar shugaban Kasar sa a zaben badi na 2026

Kemi Seba da ya yi shuhura wajen caccakar wadan su shuwagabannin Afirka da yake dangantawa da karnukan farautar turawan yamma ya bayyana wannan aniya tasa ne ta kafar shafukan sada zumunta na zamani ta cikin wani faifen bidiyo da ya wallafa.

Dan fafutikar ya kuma yi fice wajen sukar salon mulkin wadan su shuwagabannin kasashen Afirka tare da yaba wa da salon kamun ludayyin shuwagabannin kasashen uku na kungiyar AES.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara