DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaro sun kama tsigaggen shugaban Korea ta Kudu

-

Jami’an tsaro a kasar Korea ta Kudu , sun kama tsigaggen shugaban kasar Yoon Suk Yeol bayan da suka kutsa inda ya samu mafaka tare da kama shi.
Kamawar ta shi ta sa ya zama shugaban kasar na farko da ke kan mulki da Jami’an tsaro masu bincike na musamman suka kama.
Shugaba Yoon, mai shekaru 64 ana binciken sa ne akan saka dokar ta baci mai cike da sarkakiya a ranar 3 ga watan Disambar da ta gabata 2024, abinda ya jefa kasar cikin mummunan rikici na bore.
Kamun na shugaba Yoon, ya kawo karshen wasan buya tsakanin shugaban da Jami’an tsaron sa da na masu bincike na musamman.
Sai dai duk da tsige shugaban da Majalisar kasar tayi shugaban na cigaba da rike iko har sai Kotun tsarin mulkin kasar ta tabbatar da tsige shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara