DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu tilascin da muka dora wa kowa kan bayar da shaida a shari’ar badakalar aikin lantarkin Mambila – Fadar Shugaban Nijeriya

-

Fadar shugaban kasa ta musanta rahotannin dake cewa an tilasta wa tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari ko wani dan NIjeriya domin ya bayar da shaida a gaban kotun sasanta rikici dake zamanta a birnin Paris na Faransa.
Da yammacin jiya Asabar ne wata jarida ta ruwaito cewa an kai wa Buhari sammaci domin ya bayar da shaida akan rikicin da ake yi na kwangilar aikin wuta na mambila ta dala biliyan 6.
Sai dai a martani na gaggawa, mai magana da yawun Shugaba Tinubu Bayo Onanuga, ya ce wannan ba gaskiya bane, amma bai musanta cewa kotun na sauraren karar ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara