DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta Nijeriya na son a rage ƙarin kudin kira da na data zuwa kashi 10 ko su tafi kotu

-

Kungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta Nijeriya NATCOMS ta ce za ta dauki matakin shari’a kan hukumar sadarwar Nijeriya NCC, biyo bayan kin amincewar bukatar rage karin kudin kira da data daga kaso 50 zuwa kaso 10.
Yayin zantawarsa da jaridar Punch a ranar Talata, shugaban kungiyar Adeolu Ogunbanjo ya ce halin ko in kula na NCC ya jefa masu amfani da layukan sadarwa cikin zulumi na karin kudaden.
“Mun basu zuwa jiya Talata cewa su fada mana matsayarsu amma har yanzu shiru, ba don haka zamu garzaya zuwa kotu a yau Laraba” in ji Adeolu.
Kungiyar ta NATCOMS na wakiltar al’ummar Nijeriya Miliyan 157 dake amfani da layukan sadarwa daban-daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An dage jana’izar marigayi Muhammad Buhari zuwa ranar Talata -Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da shirye-shiryen jana'izar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga Yuli,...

Jam’iyyar ADC ta sanar da kwana uku na alhinin rashin tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari

Jam’iyyar ADC ta bayyana kwanaki uku na zaman makoki ga mambobinta don girmama marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi...

Mafi Shahara