DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin Nijeriya ta ce sojoji sunyi ajalin ‘yan ta’adda 358 tare da kama 431 a cikin watan Janairun 2025

-

CDS Christopher Musa

Google search engine

Daraktan yada labarai na rundunar Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana hakan, a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, inda ya ce rundunar na ci gaba kai hare hare ga ‘yan ta’adda da masu tada kayar baya a fadin kasar.

A cewar sanarwar sojojin sun kama mutane 59 da suka aikata laifin satar mai tare da ceto mutane 249 da aka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta kuma kara da cewa sojojin sun kwato makamai 370 da alburusai 4,972 da suka hada da bindigogi kirar AK47 guda 105, bindigogi kirar gida guda 25, da karin wasu bindigogin guda 32, da kuma albarusai 3,066.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban layin wutar lantarkin Nijeriya National Grid ya fadi

Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya fadi Litinin din nan, lamarin da ya jefa ’yan Nijeriya da dama cikin duhu bayan da manyan tashoshin...

‘Yan bindiga sun kai hari a wani kauye na jihar Kebbi

’Yan bindiga sun kai hari a kauyen Gebbe da ke karamar hukumar Shanga a jihar Kebbi, inda rahotanni ke nuna an rasa rayuka yayin da...

Mafi Shahara