DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Bola Tinubu ya amince da a kashe naira biliyan 80 wajen fadada madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Ministan albarkatun ruwa Farfesa Joseph Utsev, ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan taron majalisar zartaswa ta kasa FEC a ranar Talata.

Utsev, wanda kuma shi ne shugaban kwamitin ma’aikatun da ke kula da madatsun ruwa, ya bayyana cewa shugaban kasar ya amince da gyaran madatsar ruwa ta Alau, bayan tattaunawa da aka yi bisa bukatar hakan.

Kwamitin, wanda aka kafa a ranar 23 ga Satumba, 2024, ya hada da ministocin kudi, muhalli, ayyuka, yada labarai, da kuma mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro a matsayin mambobi.

An kaddamar da kwamitin ne a ranar 2 ga Oktoba, 2024 da nufin tantance madatsun ruwa a fadin kasar tare da ba da shawarar ingantasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya ja layi da wanda ba sa goyon bayan Tinubu

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce zai mara wa duk dan takarar da ke goyon bayan Shugaban Kasa, Bola Tinubu, baya a...

Tinubu zai kai ziyara jihar Adamawa a ranar Litinin

Shugaban kasa, Bola Tinubu, zai kai ziyara ta aiki jihar Adamawa ranar Litinin, kasa da sa’o’i 48 bayan irin wannan ziyara da ya kai a...

Mafi Shahara