DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babbar Kotu a Abuja ta fidda ranar fara sauraron karar da aka shigar kan Wike

-

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 18 ga watan Fabrairu domin ci gaba da sauraron karar da wasu mabarata da marasa galihu suka shigar kan Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike inda suke kalubalantar kama su da tsare su. 

Tun da farko, lauyan wadanda suka shigar da karar, Usman Chamo, ya shaida wa kotun cewa har yanzu ana ci gaba da cin zarafin wadanda yake karewa a babban birnin tarayya Abuja, inda ya ce Wike na yaki da barace-barace a yankin.

Google search engine

Saidai Yayin da yake dage sauraren karar mai shari’a James Omotosho a ranar Talata ya sanya ranar 18 ga wata a matsayin lokacin da za fara sauraron karar 

Ya kuma ba da umarnin aikewa da takardun kotun zuwa ga Sufeto Janar na ‘yan sanda, Hukumar Tsaro ta farin kaya (NSCDC), da kuma Babban Lauyan Tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara