DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babbar Kotu a Abuja ta fidda ranar fara sauraron karar da aka shigar kan Wike

-

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 18 ga watan Fabrairu domin ci gaba da sauraron karar da wasu mabarata da marasa galihu suka shigar kan Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike inda suke kalubalantar kama su da tsare su. 

Tun da farko, lauyan wadanda suka shigar da karar, Usman Chamo, ya shaida wa kotun cewa har yanzu ana ci gaba da cin zarafin wadanda yake karewa a babban birnin tarayya Abuja, inda ya ce Wike na yaki da barace-barace a yankin.

Google search engine

Saidai Yayin da yake dage sauraren karar mai shari’a James Omotosho a ranar Talata ya sanya ranar 18 ga wata a matsayin lokacin da za fara sauraron karar 

Ya kuma ba da umarnin aikewa da takardun kotun zuwa ga Sufeto Janar na ‘yan sanda, Hukumar Tsaro ta farin kaya (NSCDC), da kuma Babban Lauyan Tarayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

SGF George Akume ya angwance da tsohuwar matar Ooni na Ife Gimbiya Zainab

Sakataren Gwamnatin Nijeriya (SGF), Sanata George Akume, ya auri Sarauniya Zaynab Ngohemba, tsohuwar matar Ooni na Ife, Oba Adeyeye Enitan Ogunwusi.   Jaridar Punch ta ce an...

Jirgin yakin Nijeriya da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal

Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya ta tabbatar da cewa jirgin ta kirar C-130 mai lamba NAF 913 ya isa cibiyar gyara jirage ta OGMA da...

Mafi Shahara