DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ko kujerar Sanata ba za ka iya ci a jihar Kaduna ba – Fadar shugaban kasa ta sake yi wa El-Rufa’i martani

-

Google search engine
Mai bai wa shugaban Nijeriya Bola Tinubu shawara kan yada labarai Daniel Bwala, yayi zazzafan martanin ga Nasir El’rufa’i inda yace ko kujerar Sanata Nasiru Elrufa’i ba zai iya ci a Kaduna ba, domin siyasarsa ta labewa cikin rigar wani jagora ce.
Bwala ya yi martanin ne a wata fira da gidan talabijin na TVC, inda ya ce tasirin siyasar El-Rufai yana da nasaba da hadakarsa da wasu jagorori, nasarar da El’rufa’i ya samu a siyasa har ya zama gwamnan Kaduna, ya laɓe ne da guguwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari kuma saboda Buhari ne aka sake zabensa karo na biyu, a don haka a yanzu ba zai iya cin zaben ko da Sanata ba.
A ‘yan kwanakinnan dai tsohon gwamnan jihar Kaduna na yawan sukar gwmnatin shugaba Tinubu da kuma jam’iyyar APC, duk da kasancewarsa dan jami’yyar.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara