HomeLabaraiIPMAN ta yi barazanar shiga yajin aiki kan rashin biyan ta bashin...

IPMAN ta yi barazanar shiga yajin aiki kan rashin biyan ta bashin Naira biliyan 100 a Nijeriya

-

 

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta a Nijeriya ta yi barazanar rufe gidajen man fetur a fadin kasar nan da sati daya idan hukumar kula da harkokin man fetur ta kasa NMDPRA ta gaza biyan mambobinsu Naira biliyan 100 na alawus-alawus ga hukumar.

Wannan dai na a cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar ga manema labarai a Abuja ranar Litinin.

Shugaban kungiyar Yahaya Alhassan, ya bayyana matukar takaicinsa kan abin da ya bayyana a matsayin sakaci da gangan da hukumar NMDPRA ta yi, duk kuwa da alkawuran da ta sha yi na warware basussukan.

A cewar Yahaya Alhassan, NMDPRA ta tabbatar wa IPMAN a wajen wani taron masu ruwa da tsaki da kungiyar masu motocin haya ta Najeriya NARTO, ta shirya cewa za ta biya kudaden a cikin kwanaki 40.

Ya kara da cewa yan kasuwan mai na cikin mawuyacin hali sakamakon rashin biyan su hakkokinsu.

Shugaban ya ce jinkirin rashin biyan alawus din ya gurgunta ayyuka a depots na Arewa guda tara da suka hada da Jos, Gusau, Minna, Suleja, Kaduna, Kano, Gombe, Yola, da Maiduguri.

Kungiyar ta kuma nuna rashin jin dadin ta kan harajin kashi biyar cikin 100 da NMDPRA ta dorawa mambobinta idan za’a sayar da gidajen man fetur, wanda suka bayyana a matsayin wanda ya sabawa tsarin mulki da ci gaban kasa.

“Ba za mu yi jinkirin daukar matakai ba idan har ba a biya mu bukatunmu ba daga yau Litinin 24 ga Fabrairu, 2025.

“Idan ba su biya mana kudaden mu ba nan da kwanaki bakwai, za mu da katar da ayyukanmu a duk fadin Nijeriya”.

Kungiyar ta IPMAN ta yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya shiga tsakani kan takaddamar da ta ki ci taki cinyewa, ta kuma bukaci mambobinta da su jajirce wajen bin doka da oda yayin da suke jiran a biya su hakkokinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img