Daya daga cikin lauyoyin da ke kare Sanata Natasha ya zargi gwamnatin jihar Kogi da daukar nauyin kiranyen da ake yunkurin yi wa Sanatar da ta fito daga Kogi ta tsakiya.
Lauyan wanda ke jawabi a gidan talabijin na Channels, ya zargi daya daga cikin hadiman gwamnatin jihar mai suna Charity Omole da daukar nauyin kiranyen.
A ranar Litinin, 24 ga watan Maris na shekarar 2025, Omole ya jagoranci wasu daga cikin mazabar sanatar daga Kogi ta Tsakiya suka gabatar da koken kiranye ga hukumar zabe mai zaman kanta wato INEC.