DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sanata Barau ya gana da gwamnan Edo kan hallaka matafiya a Uromi, yayin da ake shirin tura wadanda aka kama zuwa Abuja

-

 

Google search engine

Gwamna jihar Edo Monday Okpebholo ya kai ziyarar jaje ga mataimakin shugaban majalisar dattawa Sanata Barau I Jibrin bisa hallaka matafiya a garin Uromi da ke jihar Edo a makon da ya gabata.

Mataimaki na musamman ga Sanata Barau kan harkokin yada labarai Alhaji Ismail Mudashir, ya ce gwamnan ya mika ta’aziyyarsa ga mataimakin shugaban majalisar, inda ya yi alkawarin cewa gwamnatin jihar Edo za ta taimaka wa iyalan wadanda lamarin ya shafa.

Gwamnan jihar Edo ya bayyana cewa mutane 14 da ake zargi da hannu a kashe matafiyan da ba su ji ba ba su gani ba, ana shirin kai su a Abuja domin ci gaba da yi musu tambayoyi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara