DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bai kamata jami’o’in Nijeriya su rika karrama marasa ilimi da halaye na kwarai ba – Farfesa Jega

-

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya bayyana damuwarsa kan yawan jami’o’in Najeriya da ke ba da digirin kwarewa ga wasu mutane da ya bayyana su a matsayin marasa ilimi ko kuma wadanda ba su da kyakkyawar halayya.
Jega ya bayyana haka ne, yayin da yake jawabi a matsayin shugaban taro a bikin yaye dalibai karo na 14 na jami’ar NOUN a Abuja. Ya ce wannan dabi’a ta ba da digiri ba tare da la’akari da cancantar ilimi da kyawawan dabi’u ba, tana haifar da koma baya ga darajar digirorin da jami’o’in Najeriya ke bayarwa.
Farfesan ya bukaci jami’o’in Najeriya da su zama masu lura sosai wajen zaben wadanda za a ba da digiri na kwarewa, yana mai gargadin cewa wannan dabi’a na iya rage darajar wannan lambar yabo a cikin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar zabe za ta hada kai da majalisar wakilan Nijeriya domin gudanar da sahihin zabe

Shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya bayyana aniyarsa ta yin aiki tare da Majalisar Dokoki domin tabbatar da gudanar da sahihin...

Jam’iyyar APC ta kalubalanci Gwamnan Filato Mutfwang da ya bayyana masu matsa masa lamba ya bar PDP

Jam’iyyar APC ta jihar Filato ta kalubalanci Gwamna Caleb Mutfwang da ya fito fili ya bayyana sunayen mutanen da ke matsa masa lamba ya bar...

Mafi Shahara