Bai kamata jami’o’in Nijeriya su rika karrama marasa ilimi da halaye na kwarai ba – Farfesa Jega

-

Tsohon Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), Farfesa Attahiru Jega, ya bayyana damuwarsa kan yawan jami’o’in Najeriya da ke ba da digirin kwarewa ga wasu mutane da ya bayyana su a matsayin marasa ilimi ko kuma wadanda ba su da kyakkyawar halayya.
Jega ya bayyana haka ne, yayin da yake jawabi a matsayin shugaban taro a bikin yaye dalibai karo na 14 na jami’ar NOUN a Abuja. Ya ce wannan dabi’a ta ba da digiri ba tare da la’akari da cancantar ilimi da kyawawan dabi’u ba, tana haifar da koma baya ga darajar digirorin da jami’o’in Najeriya ke bayarwa.
Farfesan ya bukaci jami’o’in Najeriya da su zama masu lura sosai wajen zaben wadanda za a ba da digiri na kwarewa, yana mai gargadin cewa wannan dabi’a na iya rage darajar wannan lambar yabo a cikin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara