DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar ya yi fatali da matakin gwamnonin PDP na kin amincewa da yin haɗaka

-

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya dage cewa hadin gwiwa tsakanin jam’iyyu ita ce kawai hanyar da za su iya kayar da shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027.
Atiku ya nuna adawa da matsayin gwamnonin jam’iyyar PDP wadanda suka nisanta jam’iyyar daga kawancen da tsohon mataimakin shugaban kasar ke shirin yi.
A ranar Litinin, kungiyar gwamnonin PDP karkashin jagorancin gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, sun bayyana cewa jam’iyyar ba za ta shiga cikin wata hadaka da kowace jam’iyya ba.
Sai dai a martanin da ya mayar, Atiku Abubakar ta hannun mataimakinsa kan yaɗa labarai Paul Ibe, ya jaddada bukatar fadada tattaunawa domin samun tattaunawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara