Gwamnan jihar Yobe Mai Mala Buni ya ce ba ya cikin kawancen shugabannin adawa da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ke jagoranta.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Mamman Mohammed, ya fitar a Damaturu ranar Asabar.
Kamfanin dillancin labaran na Nijeriya ya bayar da rahoton cewa wani labari da yake yawo Gwamna Mai Mala Buni da wasu gwamnonin APC hudu sun kammala shirye-shiryen sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa ta PDP da kuma shiga jam’iyyar kafin zaben 2027.
Sai dai Mamman ya bayyana labarin matsayin kage kuma baya da tushe.
Ya ce wanda ya bayar da labarin bai da wani kusanci da gwamnan balle ya bayar da labarin yana shirin sauya sheka zuwa wata jam’iyya.



