DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC za ta dare gida biyu; su Ganduje ma duk za su koma PDP – Sule Lamido

-

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana cewa akwai yiyuwar jam’iyyar APC mai mulki za ta rabu nan ba da jimawa ba, tare da yiwuwar shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, da wasu shugabanni su sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.

Sule Lamido, wanda shi ne tsohon ministan harkokin waje na Nijeriya kuma jigo a jam’iyyar PDP, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin musamman a taron gangamin jam’iyyar PDP da aka gudanar a dandalin Aminu Kano da ke jihar Jigawa.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa shugabanni da dama na jam’iyyar PDP ciki ha da sanatoci, gwamnoni, ‘yan majalisar wakilai da sauransu sun sauya sheka zuwa APC a shirye-shiryen zaben 2027.

Sai dai a martaninsa, daraktan yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Bala Ibrahim, ya shaida wa Daily Trust cewa mafarki ne kawai jam’iyyar PDP ke yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara