DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC za ta dare gida biyu; su Ganduje ma duk za su koma PDP – Sule Lamido

-

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana cewa akwai yiyuwar jam’iyyar APC mai mulki za ta rabu nan ba da jimawa ba, tare da yiwuwar shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje, da wasu shugabanni su sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP.

Sule Lamido, wanda shi ne tsohon ministan harkokin waje na Nijeriya kuma jigo a jam’iyyar PDP, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin musamman a taron gangamin jam’iyyar PDP da aka gudanar a dandalin Aminu Kano da ke jihar Jigawa.

Jaridar Daily Trust ta ba da labarin cewa shugabanni da dama na jam’iyyar PDP ciki ha da sanatoci, gwamnoni, ‘yan majalisar wakilai da sauransu sun sauya sheka zuwa APC a shirye-shiryen zaben 2027.

Sai dai a martaninsa, daraktan yada labarai na jam’iyyar APC na kasa, Bala Ibrahim, ya shaida wa Daily Trust cewa mafarki ne kawai jam’iyyar PDP ke yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kai ne babban ‘butulu’, sakon NNPP ga Kwankwaso in ji jaridar Punch

Jam’iyyar NNPP ta soki Engr Rabiu Kwankwaso bisa kiran wasu ‘yan Kwankwassiyya da suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC da sun yi butulci, jam'iyyar tana...

Tattalin arzikin Nijeriya na kara bunkasa duk kuwa da hauhawar farashin kaya – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa tattalin arzikin Nijeriya na bunkasa a cikin kusan shekaru goma a shekarar 2024. Hakan na zuwa ne sakamakon kyakkyawan ci gaba...

Mafi Shahara