DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matakan da Shugaba Tinubu ke dauka sun taimaka wajen rage talauci a Arewacin Nijeriya – Gwamna Uba Sani

-

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya bayyana cewa babu wata gwamnati a tarihin Nijeriya da ta zuba jari a harkar noma kamar yadda gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi cikin shekaru biyu da suka gabata.

Gwamna Uba Sani ya ce matakan da Tinubu ya dauka sun taimaka matuka wajen rage talauci a Arewacin kasar.

Google search engine

Uba Sani ya jaddada irin goyon bayan da ake bai wa kananan manoma, tallafin takin zamani, da kuma taimakon kudi ba tare da la’akari da jam’iyya ba ga jihohi.

Ya danganta wadannan kokari da cike gibin ababen more rayuwa, samar da ayyukan yi, da kuma rage talauci a cikin al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara