DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Donald Trump ya kai ziyarar aiki a Saudiyya

-

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya isa Saudiyya a wata ziyara ta kwanaki hudu a yankin Gulf mai arzikin man fetur, inda zai mayar da hankali kan yarjejeniyoyin tattalin arziki da batutuwan tsaron yankin.

Batutuwan sun hada da yakin Gaza da tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran.

Google search engine

Trump na tare da fitattun shugabannin kasuwanci daga Amurka a ziyarar, inda zai fara da ziyartar Riyadh, inda ake gudanar da taron Saudi-U.S. Investment Forum, kafin ya wuce Qatar ranar Laraba da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa ranar Alhamis.

Ba ya da shirin tsayawa a Isra’ila, abin da ya tayar da tambayoyi game da matsayin wannan kasa abokiyar Amurka a cikin jerin fifikon siyasar Amurka.

Trump na fatar samun zuba jari na tiriliyoyin daloli daga kasashen da ke samar da mai a yankin Gulf.

Saudiyya ta yi alkawarin zuba jarin Dalar Amurka bilyan 600, amma Trump ya bayyana cewa yana son dala tiriliyan 1 daga Saudiyya, wadda ke daga cikin manyan abokan huldar Amurka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara