DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Shugaba Tinubu ta bukaci bankin musulunci da ya kara zuba jari a kasuwar abincin halal a Nijeriya

-

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shatima ne ya bayyana buƙatar a yayinda ya yi wata ganawa da tawagar bankin a fadar Shugaban Kasa,

Mataimakin shugaban yayi nuni da yadda Najeriya ta sami bunkasa a harkokin kasuwanci a karkashin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu da irin kokarin da gwamnati ke yi na magance kalubalen da ake fuskanta a muhimman ɓangarorin tattalin arziki da suka hadar da zuba jari akan ƴan kasa da samar da abinci mai gina jiki, da bunkasa noma, da kiwon lafiya, da ilimi, da kasuwanci na zamani inda ya karfafa wa bankin gwiwar kan yin amfani da yanayin da ake ciki a matsayin lokaci mafi dacewa na zuba jari a Najeriya, yana mai nuni da sauye-sauye a sassa masu mahimmanci da gwamnatin ta samar

Google search engine

Baya da bunkasa tattalin arzikin Halal, Kashim Shettima ya bukaci bankin da ya inganta kasuwanci a bangaren fasahar zamani, da hada-hadar kudi da sabon shirin Agro-Processing Zones (SAPZ) na samar da muhalli na musamman ga noma da ilmi da ababen more rayuwa da kiwon lafiya.

Ita ma Tawagar bankin Musulunci, karkashin jagorancin Mista Hammad Hundal, ta nuna gamsuwarta da tsare-tsaren gwamnatin shugaba Tinubu inda ta bayyana kudurinta na fifita ƙudurorin Shugaban a matsayin hanyar haɓaka farfado da walwala da magance talauci, da kuma haifar da ci gaban tattalin arziƙin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Amurka ta mayar wa China da martani kan gargadin harin soja a Nijeriya

Wani ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya caccaki China saboda gargadin da ta yi wa Washington kan yiwuwar harin soja a Nijeriya bisa zargin...

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

Mafi Shahara