DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tafi da ‘yan jaridar Nijar zuwa Yamai bayan kama su da sojin mulkin kasar suka yi

-

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun tusa kewar ‘yan jaridar uku na Radio Sahara da suka kama a Agadez zuwa babban birnin Yamai.

Jami’an tsaron Gendarmerie na jihar Agadez sun yi wa ‘yan jaridar uku na Radio Sahara rakiya zuwa babban birnin Yamai bayan sun kwashe kwanaki hudu a tsare a hannun gendarmerie.

Google search engine

‘Yan jaridar dai uku da suka hada Hamid Mahmoud, Masaouda Jaharou da kuma Mahaman Sani an kama su ne da farko a daren 7 wayewar 8 ga watan Mayun nan biyo bayan yada wani labari da ke nuna cewa Nijar ta katse dangantakar tsaro da kasar Rasha.

An dai kuma saki ‘yan jaridar a ranar 9 ga watan Mayun bayan an gurfanar da su a gaban kotun jihar Agadez sai dai a daren wannan rana ta 9 wayewar 10 ga watan Mayun kuma jami’an tsaron Gendarmerie sun sake kama su da misalin karfe 3 na dare inda suka shafe kwanaki 4 kafin a yau a tusa kewar su zuwa babban birnin Yamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara