DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tafi da ‘yan jaridar Nijar zuwa Yamai bayan kama su da sojin mulkin kasar suka yi

-

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun tusa kewar ‘yan jaridar uku na Radio Sahara da suka kama a Agadez zuwa babban birnin Yamai.

Jami’an tsaron Gendarmerie na jihar Agadez sun yi wa ‘yan jaridar uku na Radio Sahara rakiya zuwa babban birnin Yamai bayan sun kwashe kwanaki hudu a tsare a hannun gendarmerie.

‘Yan jaridar dai uku da suka hada Hamid Mahmoud, Masaouda Jaharou da kuma Mahaman Sani an kama su ne da farko a daren 7 wayewar 8 ga watan Mayun nan biyo bayan yada wani labari da ke nuna cewa Nijar ta katse dangantakar tsaro da kasar Rasha.

An dai kuma saki ‘yan jaridar a ranar 9 ga watan Mayun bayan an gurfanar da su a gaban kotun jihar Agadez sai dai a daren wannan rana ta 9 wayewar 10 ga watan Mayun kuma jami’an tsaron Gendarmerie sun sake kama su da misalin karfe 3 na dare inda suka shafe kwanaki 4 kafin a yau a tusa kewar su zuwa babban birnin Yamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada mahajjaci ya rike kudin da suka wuce Riyal 60,000 a kasar Saudiyya – Jan hankalin NAHCON ga Alhazan Nijeriya

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta shawarci mahajjatan kasar da su guji daukar kudi sama da Riyal 60,000 na Saudiyya domin...

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

Mafi Shahara