DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An tafi da ‘yan jaridar Nijar zuwa Yamai bayan kama su da sojin mulkin kasar suka yi

-

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun tusa kewar ‘yan jaridar uku na Radio Sahara da suka kama a Agadez zuwa babban birnin Yamai.

Jami’an tsaron Gendarmerie na jihar Agadez sun yi wa ‘yan jaridar uku na Radio Sahara rakiya zuwa babban birnin Yamai bayan sun kwashe kwanaki hudu a tsare a hannun gendarmerie.

Google search engine

‘Yan jaridar dai uku da suka hada Hamid Mahmoud, Masaouda Jaharou da kuma Mahaman Sani an kama su ne da farko a daren 7 wayewar 8 ga watan Mayun nan biyo bayan yada wani labari da ke nuna cewa Nijar ta katse dangantakar tsaro da kasar Rasha.

An dai kuma saki ‘yan jaridar a ranar 9 ga watan Mayun bayan an gurfanar da su a gaban kotun jihar Agadez sai dai a daren wannan rana ta 9 wayewar 10 ga watan Mayun kuma jami’an tsaron Gendarmerie sun sake kama su da misalin karfe 3 na dare inda suka shafe kwanaki 4 kafin a yau a tusa kewar su zuwa babban birnin Yamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara