DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun ba karnukansu jarirai ‘yan biyu da aka haifa a lokacin da suke tsare da mahaifiyarsu – Hon Sani Jaji

-

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kaura Namoda da Birnin Magaji a jihar Zamfara, Hon. Aminu Sani Jaji, ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ke addabar yankin Arewa maso Yamma sun ba karnukansu wasu jarirai ‘yan biyu da aka haifa a lokacin da Barau n dajin ke tsare da mahaifiyarsu.

Yayin wata tattaunawa da manema labarai, Jaji ya ce an sace wata mata daga wani gari a jihar Zamfara tana dauke da juna biyu.

Ya ce bayan da matar ta haifi ‘yan biyu, sai ‘yan bindigar suka jefa jariran ga karnuka, inda suka cinye su.

Hon Sani Jaji ya ce wannan shi ne matakin rashin imani da rashin tausayi da yankin ke fama da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kada mahajjaci ya rike kudin da suka wuce Riyal 60,000 a kasar Saudiyya – Jan hankalin NAHCON ga Alhazan Nijeriya

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta shawarci mahajjatan kasar da su guji daukar kudi sama da Riyal 60,000 na Saudiyya domin...

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

Mafi Shahara