DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun ba karnukansu jarirai ‘yan biyu da aka haifa a lokacin da suke tsare da mahaifiyarsu – Hon Sani Jaji

-

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kaura Namoda da Birnin Magaji a jihar Zamfara, Hon. Aminu Sani Jaji, ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ke addabar yankin Arewa maso Yamma sun ba karnukansu wasu jarirai ‘yan biyu da aka haifa a lokacin da barayin dajin ke tsare da mahaifiyarsu.

Yayin wata tattaunawa da manema labarai, Jaji ya ce an sace wata mata daga wani gari a jihar Zamfara tana dauke da juna biyu.

Google search engine

Ya ce bayan da matar ta haifi ‘yan biyu, sai ‘yan bindigar suka jefa jariran ga karnuka, inda suka cinye su.

Hon Sani Jaji ya ce wannan shi ne matakin rashin imani da rashin tausayi da yankin ke fama da shi.

1 COMMENT

  1. Wannan lamari da mai ya yi kama!!!
    Wallahi Allah ya Isa, ba mu yafe ba.
    Ba yadda za a yi mu zauna lafiya,matuqar Shuwagabannin mu ba su dauki mataki ba.
    Allah Dan Hasken Fuskar wannan Annabi na Ka SAW 🤲🤲🤲🤲DUK Mai hannu ✋✋ aciki Allah kai ma na Maganin su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara