DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun saci wani shugaban jam’iyyar APC, sun nemi a ba su kudin fansa Naira milyan 100

-

Wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wani shugaban jam’iyyar APC na gundumar Ward 5 da ke Ifon, a karamar hukumar Ose ta jihar Ondo, Nelson Adepoyigi.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a bakin gonarsa da ke kan hanyar Ifon zuwa Owo.

Google search engine

Majiyoyi daga cikin al’umma sun ce ‘yan bindigar sun tuntubi iyalan wanda aka sace, inda suka nemi a biya su Naira miliyan 100 kafin su sako shi.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ondo, DSP Olusola Ayanlade, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da aka fitar wa manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Murabus din Ganduje wata maƙarƙashiya ce aka shirya domin cire Shettima daga gwamnatin Tinubu – Zargin wasu mutanen Borno

Wasu daga cikin al'ummar jihar Borno sun zargi murabus din Ganduje a matsayin wata maƙarƙashiya da aka shirya domin a kawar da Kassim Shettima a...

Mafi Shahara