DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun saci wani shugaban jam’iyyar APC, sun nemi a ba su kudin fansa Naira milyan 100

-

Wasu mutane da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace wani shugaban jam’iyyar APC na gundumar Ward 5 da ke Ifon, a karamar hukumar Ose ta jihar Ondo, Nelson Adepoyigi.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a bakin gonarsa da ke kan hanyar Ifon zuwa Owo.

Majiyoyi daga cikin al’umma sun ce ‘yan bindigar sun tuntubi iyalan wanda aka sace, inda suka nemi a biya su Naira miliyan 100 kafin su sako shi.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ondo, DSP Olusola Ayanlade, ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da aka fitar wa manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotu a Kano ta ki karbar bukatar Ganduje ta dakatar da shari’ar zargin cin hanci

Wata babbar kotu a jihar Kano ta yi watsi da wata bukata da shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Umar Ganduje, ya shigar domin kalubalantar...

Da kamar wuya PDP ta rayu har 2027 – Tsohon Gwamnan Benue Gabriel Suswan

Tsohon Gwamnan jihar Benue, Sanata Gabriel Suswam, ya yi gargadin cewa jam’iyyar PDP na iya rushewa kafin zaben 2027 idan shugabanninta ba su dauki matakan...

Mafi Shahara