DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kamfanin Orano mai aikin hakar ma’adanan uranium ya shigar gwamnatin Nijar kara bisa kama wani babban jami’in kamfanin

-

Kamfanin Orano na kasar Faransa mai aikin hakar ma’adanan uranium a Nijar ya ce ya garzaya kotu domin domin kalubalantar kamun da gwamnatin Nijar ta yi wa wani babban jami’in kamfanin a ofishinsa da ke a birnin Yamai.

Kamfanin dai ya bayyana hakan ne a ranar 13 ga watan Mayun nan a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shainsa na yanar gizo, inda ya ce wannan kamu ya saba doka.

A cewar kamfanin tun a ranar 5 ga watan Mayu ne wasu jami’an tsaro suka kutsa ofisoshin ma’aikatansa suka kwashe na’urorin komfutoci tare da kwace wayoyin ma’aikatan.

Kamfanin ya kara da cewa, a yayin wannan samame ne da jami’an tsaron suka yi awon gaba da babban daraktan kamfanin Orano Malan Ibrahim Courmo kuma har yanzu kamfanin bai samu damar yin magana da shi ba, tsawon kwanaki takwas kenan ake tsare da shi.

Kazalika kamfanin ya ce a yanzu haka jami’an tsaron sun yi wa ofishin kamfanin kawanya.

Tun bayan juyin mulkin Yulin 2023 dai ake ta kai ruwa rana tsakanin kamfanin Orano da hukumomin mulkin sojan Nijar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Barayin daji sun ba karnukansu jarirai ‘yan biyu da aka haifa a lokacin da suke tsare da mahaifiyarsu – Hon Sani Jaji

Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kaura Namoda da Birnin Magaji a jihar Zamfara, Hon. Aminu Sani Jaji, ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da...

Akalla Mahajjatan Nijar 700 sun isa kasa mai tsarki

A ranar Talatar nan 13 ga watan Mayun 2025, rukuni biyu na farko na maniyyatan Nijar ya tashi zuwa kasa mai tsarki dauke da mutane...

Mafi Shahara