DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na bukatar dala biliyan 10 duk shekara domin samar da isashshen wutar lantarki – Ministan lantarki Adelabu.

-

By Salim Muhammad Gali

Ministan wutar lantarki na kasa Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa Nijeriya na buƙatar aƙalla dala biliyan 10 duk shekara na tsawon shekaru 20, domin samar dai isashshen wutar lantarki ga ‘yan kasar.

Google search engine

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito ministan na wannan bayanin, a yayin da yake kaddamar da tashar samar da wutar lantarki daga hasken rana mai ƙarfin megawat 2.5 a makarantar sojoji NDA da ke jihar Kaduna.

Ministan ya ce sama da shekaru 60 matsaloli sun dabaibaye bangaren lantarki da suna hada rashin isasshen saka hannun jari, rashin kiyaye kayayyakin aiki, da kuma ƙarancin inganta tsarin rarraba wutar.

Adelabu ya bayyana cewa sanya hannu kan dokar makamashi ya bai wa jihohi damar taka rawa kai tsaye a harkar samar da wuta, kama daga samarwa zuwa rabawa, kuma fiye da jihohi 11 sun fara daukar hanya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara