DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na bukatar dala biliyan 10 duk shekara domin samar da isashshen wutar lantarki – Ministan lantarki Adelabu.

-

By Salim Muhammad Gali

Ministan wutar lantarki na kasa Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa Nijeriya na buƙatar aƙalla dala biliyan 10 duk shekara na tsawon shekaru 20, domin samar dai isashshen wutar lantarki ga ‘yan kasar.

Google search engine

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito ministan na wannan bayanin, a yayin da yake kaddamar da tashar samar da wutar lantarki daga hasken rana mai ƙarfin megawat 2.5 a makarantar sojoji NDA da ke jihar Kaduna.

Ministan ya ce sama da shekaru 60 matsaloli sun dabaibaye bangaren lantarki da suna hada rashin isasshen saka hannun jari, rashin kiyaye kayayyakin aiki, da kuma ƙarancin inganta tsarin rarraba wutar.

Adelabu ya bayyana cewa sanya hannu kan dokar makamashi ya bai wa jihohi damar taka rawa kai tsaye a harkar samar da wuta, kama daga samarwa zuwa rabawa, kuma fiye da jihohi 11 sun fara daukar hanya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara