DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na bukatar dala biliyan 10 duk shekara domin samar da isashshen wutar lantarki – Ministan lantarki Adelabu.

-

By Salim Muhammad Gali

Ministan wutar lantarki na kasa Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa Nijeriya na buĆ™atar aĆ™alla dala biliyan 10 duk shekara na tsawon shekaru 20, domin samar dai isashshen wutar lantarki ga ‘yan kasar.

Gidan talabijin na Channels ya ruwaito ministan na wannan bayanin, a yayin da yake kaddamar da tashar samar da wutar lantarki daga hasken rana mai ƙarfin megawat 2.5 a makarantar sojoji NDA da ke jihar Kaduna.

Ministan ya ce sama da shekaru 60 matsaloli sun dabaibaye bangaren lantarki da suna hada rashin isasshen saka hannun jari, rashin kiyaye kayayyakin aiki, da kuma ƙarancin inganta tsarin rarraba wutar.

Adelabu ya bayyana cewa sanya hannu kan dokar makamashi ya bai wa jihohi damar taka rawa kai tsaye a harkar samar da wuta, kama daga samarwa zuwa rabawa, kuma fiye da jihohi 11 sun fara daukar hanya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi kuskure a sakamakon da muka fitar na dalibai – Hukumar JAMB

Cikin alhini da nadamar abin da ya faru, hukumar JAMB da ke shirya jarabawar neman shiga makarantun gaba da sakandare a Nijeriya ta karbi duk...

An tafi da ‘yan jaridar Nijar zuwa Yamai bayan kama su da sojin mulkin kasar suka yi

Hukumomin mulkin sojan Nijar sun tusa kewar 'yan jaridar uku na Radio Sahara da suka kama a Agadez zuwa babban birnin Yamai. Jami'an tsaron Gendarmerie na...

Mafi Shahara