Hukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA, ta yi kira ga jihohin kasar da su zamo cikin shiri domin tunkarar ambaliyar ruwa da ke iya afkuwa a daminar bana, 2025.
Hukumar ta ce za ta aika tawaga kowace Jiha domin tattataunawa da al’ummar da ake sa ran faruwar ambaliyar domin gargadi da kuma zama cikin shirin ko-ta-kwana.
Darakta Janar ta NEMA, Malama Zubaida Umar ce ta bayyana hakan a wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a Abuja.
Sai dai, hukumar ta NEMA ba ta ambaci sunayen jihohi da kananan hukumomin da ake sa ran ambaliyar ruwan za ta afku ba.




Ubangiji allah ya kara tsaremuena imaninmu,
Allah ka karama
Annabi daraja S.A.W
DLC
Allah ya kara basira.