DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Daliban da suka rubuta jarabawar JAMB sun nemi da a soke sakamakon da aka fitar

-

Wasu daga cikin daliban da suka rubuta jarabawar JAMB da ke ba da damar samun gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandare ta shekarar 2025 sun bukaci a soke sakamakon jarabawar gaba daya.

Sun bayyana hakan ne a hirarsu da jaridar Daily Trust, a martaninsu ga amincewar Hukumar JAMB cewa an samu kura-kurai da suka shafi yadda dalibai suka fuskanci jarabawar.

Google search engine

An sha korafe-korafe daga sassa daban-daban na Nijeriya game da rashin kyakkyawan sakamako, inda sama da dalibai milyan 1.5 suka kasa samun maki 200. Wasu sun danganta hakan da matsalolin fasaha a wasu cibiyoyin jarabawa, yayin da wasu ke zargin rashin tsara lokaci da kuma rashin isasshen shiri daga bangaren dalibai.

Shugaban hukumar JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya fashe da kuka a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja, yayin da yake bayar da hakuri kan kura-kuran da suka shafi jarabawar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara