DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Daliban da suka rubuta jarabawar JAMB sun nemi da a soke sakamakon da aka fitar

-

Wasu daga cikin daliban da suka rubuta jarabawar JAMB da ke ba da damar samun gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandare ta shekarar 2025 sun bukaci a soke sakamakon jarabawar gaba daya.

Sun bayyana hakan ne a hirarsu da jaridar Daily Trust, a martaninsu ga amincewar Hukumar JAMB cewa an samu kura-kurai da suka shafi yadda dalibai suka fuskanci jarabawar.

Google search engine

An sha korafe-korafe daga sassa daban-daban na Nijeriya game da rashin kyakkyawan sakamako, inda sama da dalibai milyan 1.5 suka kasa samun maki 200. Wasu sun danganta hakan da matsalolin fasaha a wasu cibiyoyin jarabawa, yayin da wasu ke zargin rashin tsara lokaci da kuma rashin isasshen shiri daga bangaren dalibai.

Shugaban hukumar JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya fashe da kuka a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja, yayin da yake bayar da hakuri kan kura-kuran da suka shafi jarabawar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara