DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta daure wani dan tiktok bayan samunsa da laifin wulakanta takardar Naira

-

Kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna karkashin mai shari’a R.M. Aikawa ta yanke wa wani dan TikTok da Instagram, Muhammad Kabir, hukunci bayan samunsa da laifin wulakantawa da lalata takardun kudi na Naira.

A cewar Shugaban Sashen Yada Labarai na hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa a Nijeriya, Dele Oyewale, an kama Kabir ne a ranar Talata, 29 ga Mayu, 2025 a Tudun Wada, Jihar Kaduna, bayan ya wallafa wani bidiyo a shafukan sa na TikTok da Instagram mai dauke da sunan @youngcee0066, inda aka gan shi yana watsi da takardun Naira a kasa, yana tattakawa, tare da fadin wasu kalamai a harshen Hausa yana kalubalantar EFCC da ta zo ta kama shi a inda yake.

Google search engine

An kama shi ne bisa karya dokar babban bankin Nijeriya CBN wadda ta haramta wulakantawa da lalata takardun kudi na Naira.

Alkalin kotun, Mai shari’a Aikawa, ya yanke wa Muhammad hukuncin dauri na wata shida 6 ko kuma ya biya tara ta Naira Dubu Dari Uku N300,000.00 ga Gwamnatin Tarayyar Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Jami’an soji za su fuskanci ritayar dole bayan sauye-sauye a fannin tsaron Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai manyan jami'an sojin Nijeriya  masu mukamin Janar akalla 60 da za su fuskanci ritayar dole, biyo bayan sauye-sauyen da...

Rashin gogewar siyasa ta sa ban tsayar da El-Rufa’i don ya gaje ni ba – Obasanjo

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ya ki tsayar da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Elrufa'i don ya gaje a shekarar 2007...

Mafi Shahara