DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda a jihar Nasarawa sun kama wata mata da makamai za ta kai su Katsina

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta bayyana cewa jami’anta, sun kama wata mata da ake zargi da safarar makamai ga barayin daji.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Ramhan Namsel ya ce, an kama Fatima Salisu mai kimanin shekaru 21 ‘yar asalin garin Funtua da ke a jihar Katsina bayan samun bayanan sirri a yankin Azuba da ke a Lafia.

Google search engine

Ana zargin Fatima ne da safarar albarusai daga jihar Nasarawa zuwa ga wasu barayin daji a Jihar Katsina.

Yanzu haka dai, wacce ake zargin na hannun jami’an tsaro domin ci-gaba da bincike da tuhumarta don gano wadanda ke da alaka da makaman.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara