DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sanda a jihar Nasarawa sun kama wata mata da makamai za ta kai su Katsina

-

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta bayyana cewa jami’anta, sun kama wata mata da ake zargi da safarar makamai ga barayin daji.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Ramhan Namsel ya ce, an kama Fatima Salisu mai kimanin shekaru 21 ‘yar asalin garin Funtua da ke a jihar Katsina bayan samun bayanan sirri a yankin Azuba da ke a Lafia.

Ana zargin Fatima ne da safarar albarusai daga jihar Nasarawa zuwa ga wasu barayin daji a Jihar Katsina.

Yanzu haka dai, wacce ake zargin na hannun jami’an tsaro domin ci-gaba da bincike da tuhumarta don gano wadanda ke da alaka da makaman.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sabon Paparoma ya gayyaci Shugaba Tinubu zuwa Rome, Italy

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amsa goron gayyatar da sabon Paparoma Pope Leo XIV ys yi masa zuwa birnin Rome na kasar Italy. Daga cikin tawagar...

Da yiwuwar a samu ambaliyar ruwa a jihohi 12 na Nijeriya – NEMA

Hukumar ba da agajin gaggawa a Nijeriya NEMA, ta yi kira ga jihohin kasar da su zamo cikin shiri domin tunkarar ambaliyar ruwa da ke...

Mafi Shahara