DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

-

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba.

Yayin da yake magana a shirin Daily Politics na Trust TV, Gilbert ya ce jam’iyyarsu ba ta da wata alaka da Kwankwaso, yana mai cewa Kwankwaso ya bar jam’iyyar NNPP tun shekarar 2023 kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Google search engine

Yayin da yake tsokaci kan yawaitar sauya sheka da ‘yan manyan jam’iyyun adawa ke yi a kasar, ciki har da NNPP, Gilbert ya ce, “Kwankwaso ya zo da mutanensa, wato masu kiran kansu Kwankwasiyya. Idan ka duba tarihin mutanen da suka fice daga jam’iyyar, za ka ga cewa sun kasance cikakkun ‘yan tafiyar Kwankwasiyya. A gaskiya, su ne suka taka muhimmiyar rawa wajen nasarar NNPP a Kano.”

Sai dai ya kara da cewa wadanda suka bar jam’iyyar NNPP sun yi hakan ne saboda sun gaji da yadda tafiyar Kwankwasiyya ke gudana, amma ba su da wata matsala da jam’iyyar NNPP kanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu babbar kyauta ne daga Allah domin gyaran Nijeriya – Yahaya Bello

Tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello ya bayyana shugaban Nijeriya Bola Tinubu a matsayin babbar kyauta da Allah ya ba Nijeriya domin gyaran kasar. Yahaya Bello...

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi. Mai...

Mafi Shahara