DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Fubara yarona ne, in ji Wike

-

Tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya bayyana wanda ya gada a mulki, Siminalayi Fubara, a matsayin “yaronsa,” a yayin da rikicin siyasa ke ci gaba tsakaninsu.

Wike, wanda yanzu haka shi ne ministan babban birnin tarayya Abuja, ya ce ko da yake Shugaba Bola Tinubu ya nemi zaman lafiya, bai yi adawa da hakan ba.

Ya ce wannan yaro nawa ne, dana ne. Yaya zan ce ina yaki da shi? Wadanda nake fada da su, su ne masu kokarin sace abin da ba su yi aiki akai ba.

“Shugaban kasa ya kira ni domin a samu sulhu; na ce masa, ‘Oga, ta yaya zaka ce in sasanta, amma in ki?’” in ji shi a wata hira da ya yi da BBC Pidgin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutum 3 tare da sace 26 a Zamfara

Akalla mutane uku ne rayukansu suka salwanta aka kuma sace wasu 26 a wani sabon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kauran Namoda...

Hadakar da nake sha’awa ita ce yaki da yunwa da Talauci a fadin Nijeriya

A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan...

Mafi Shahara