DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wike ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu a zaben 2027

-

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya musanta jita-jitar da ke yawo cewa yana iya kalubalantar Shugaba Bola Tinubu a zaben 2027 idan jam’iyyar PDP ta ware tikitin shugaban kasa zuwa Kudu.

Ya tabbatar da biyayyarsa ga gwamnatin Tinubu, yana mai cewa bai da niyyar tsayawa takara da mutumin da yake yi wa aiki.

A wata hira da ya yi da BBC News sashen Pidgin, Wike ya ce, ba zai tsaya takara ba. Ya diga alamar tambayar cewa me zai sa ya tsaya takara da wanda yake yi wa aiki?.

Yayin da yake jaddada goyon bayansa ga Tinubu, Wike ya ce a halin yanzu babu wani dan adawa mai karfi da zai iya kawar da shugaban kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutum 3 tare da sace 26 a Zamfara

Akalla mutane uku ne rayukansu suka salwanta aka kuma sace wasu 26 a wani sabon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kauran Namoda...

Hadakar da nake sha’awa ita ce yaki da yunwa da Talauci a fadin Nijeriya

A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan...

Mafi Shahara