DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutum 3 tare da sace 26 a Zamfara

-

Akalla mutane uku ne rayukansu suka salwanta aka kuma sace wasu 26 a wani sabon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kauran Namoda da ke jihar Zamfara.

Jaridar Daily Trust ta ce hare-haren da aka kai tsakanin ranakun Alhamis da Asabar, sun shafi mutane da dama.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa kauyen Sabon Gari sun sha fama da tashin hankalin na baya-bayan nan, inda aka halaka mace guda tare da yin garkuwa da mazauna yankin kusan 20.

Wani mazaunin Kauran Namoda, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya yi ikirarin cewa adadin ya zarta haka, inda ya ce an kashe mutane hudu, ciki har da mace daya, tare da sace wasu 26.

Rahotanni sun ce daga cikin wadanda aka sacen har da wani mutum, da matansa biyu, da ‘ya’yansu uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hadakar da nake sha’awa ita ce yaki da yunwa da Talauci a fadin Nijeriya

A yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar hadaka tsakanin jiga-jigan ‘yan adawa don tunkarar shugaban kasa Bola Tinubu a zaben 2027, tsohon dan...

Jami’an tsaron fadar Vatican sun hana Seyi Tinubu zuwa wurin Fafararoma a yayin bikin rantsar da shi

Jami'an Daily Trust ta ruwaito cewa a yayin ziyarar da Sheyin ya bi tawagar shugaba Tinubu, Bola Tinubu ya ganada da Peter Obi, daya daga cikin...

Mafi Shahara