DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutum 3 tare da sace 26 a Zamfara

-

Akalla mutane uku ne rayukansu suka salwanta aka kuma sace wasu 26 a wani sabon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kauran Namoda da ke jihar Zamfara.

Jaridar Daily Trust ta ce hare-haren da aka kai tsakanin ranakun Alhamis da Asabar, sun shafi mutane da dama.

Google search engine

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa kauyen Sabon Gari sun sha fama da tashin hankalin na baya-bayan nan, inda aka halaka mace guda tare da yin garkuwa da mazauna yankin kusan 20.

Wani mazaunin Kauran Namoda, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya yi ikirarin cewa adadin ya zarta haka, inda ya ce an kashe mutane hudu, ciki har da mace daya, tare da sace wasu 26.

Rahotanni sun ce daga cikin wadanda aka sacen har da wani mutum, da matansa biyu, da ‘ya’yansu uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara