DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Demokaradiyyar yamma ba ta aiki a Najeriya — Agbakoba

-

Tsohon shugaban kungiyar lauyoyi ta Nijeriya, Olisa Agbakoba SAN, ya bayyana cewa tsarin dimokuraɗiyyar da Najeriya ke amfani da shi wanda aka aro daga ƙasashen Yamma ba ya aiki, yana mai kira da a sake fasalin tsarin mulkin.

A cewarsa, bayan fiye da shekara 25 da mulkin dimokuraɗiyya, har yanzu Najeriya ba ta samu cigaba mai ma’ana ba, yana mai cewa akwai babban kuskure a tsarin da ba ya samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan ƙasa.

Agbakoba ya soki yadda ‘yan adawa ke sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC, yana cewa hakan ba zai taimaka wajen gyara demokaraɗiyya ba. Inda yace da yawa cikin ‘yan siyasa burinsu kawai shi ne su karɓi mulki, ba kula da bukatun talakawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta dakatar da sanya tallar magungunan gargajiya a cikin fim

Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano ta dakatar da dukkan tallace-tallacen magungunan gargajiya da ake nunawa a fina-finan Hausa da na masu shela da makirufo...

Shugabannin Kudu maso Gabas na shirin taron marawa Tinubu bayan tazarce a takarar 2027 — Umahi

Ministan Ayyuka kuma tsohon Gwamnan Jihar Ebonyi, Dave Umahi, ya bayyana cewa shugabannin yankin Kudu maso Gabas, ciki har da gwamnonin jihohi biyar na yankin,...

Mafi Shahara