DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ADC na shirin zama hadakar jam’iyyar ‘yan adawa don kayar da Tinubu a 2027, inji Dailytrust

-

Wani rahoton jaridar Dailytrust ya bayyana cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) na shirin zama sabuwar cibiyar hadin gwiwar manyan ‘yan adawa a Najeriya, bayan da aka amince da ita a matsayin dandalin fafutukar siyasar da za ta kalubalanci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027.

Wannan hadaka karkashin jagorancin tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party a 2023 Peter Obi, da kuma tsohon Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai, ta samu ne bayan ganawar sirri da aka yi a Abuja.

Google search engine

Rahotanni sun nuna cewa, tun da farko hadakar ta yi shirin amfani da jam’iyyar SDP, amma rikicin cikin gida da rashin yarda da sharudan da jam’iyyar ta gindaya ya sa aka fasa hakan.

Shugaban SDP, Shehu Gabam, ya bayyana cewa ba za su bari a tasirinsu ya zama na wucin gadi ba, daga ADC kuwa shugabanta Ralphs Nwosu, ya tabbatar da tattaunawa da kwamitin hadakar, yana mai cewa hadin gwiwar na neman ceto Najeriya daga halin da take ciki.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara