DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Katsina ta bukaci WAEC ta soke jarrabawar turanci da daliban jihar suka rubuta bana

-

Gwamnatin Jihar Katsina ta nemi a soke jarrabawar harshen Turanci da Hukumar WAEC ta gudanar kwanan nan, sakamakon jinkirin da aka samu a fara jarrabawar a fadin kasa.

Kwamishinar Ilimi na Firamare da Sakandare, Hajiya Zainab Musa-Musawa, ta bayyana matsayar gwamnatin ne yayin ziyararta ofishin WAEC da ke Katsina, inda ta ce an gabatar da koke a hukumance da sa hannun Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Hajiya Ummukhair Ahmed.

Google search engine

Rahoton kamfanin dillancin labaran Nijeriya ya bayyana cewa WAEC ta danganta jinkirin da kokarin dakile satar amsa ne.
Musa-Musawa ta bukaci iyaye, makarantu da al’umma su kasance masu hakuri har sai an kammala bincike kan batun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara