DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dadi nake ji idan na takalo manyan mutane – inji ministan Abuja Wike

-

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya ce yana samun farin ciki duk lokacin da ya takalo manyan mutane a kasar.

Wike, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, ya ce duk masu kadarorin da ke Abuja da har yanzu ba su biya harajin kasa na gidansu ba, inda ya kara da cewa dole ne su yi hakan ko kuma su fuskanci fushin doka.

Google search engine

Tsohon gwamnan jihar Ribas ya caccaki wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP da suka hada da Bode George, yana mai cewa dole ne PDP ta biya harajin ofishinta da ke Abuja.

Wike ya ce magabatansa da suka jagoranci babban birnin tarayya Abuja ciki har da gwamnan jihar Bauchi a yanzu Bala Mohammed, sun kasa tilasta jiga-jigan ‘yan siyasa wadanda suka mallaki gine-gine a Abuja su rika biyan kudin harajin gidajensu na shekara-shekara.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili shi ne Mataimakin Editan Gudanarwa kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki na DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin tabbatar da inshorar lafiya a dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnatin Nijeriya

Shugaba Bola Tinubu ya umarci sakataren gwamnatin tarayya da ya fitar da takardar umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomi domin tabbatar da inshorar lafiya bisa...

Zan iya kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga cikin watanni biyu muddin na samu iko da hukumomin tsaro – Gwamnan Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa matsalar ayyukan ’yan bindiga da ke addabar jihar za ta zama tarihi muddin ya samu damar bayar da...

Mafi Shahara