DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rokonmu ga Saudiyya na neman sake ba da ‘Visar’ aikin hajjin 2025 bai yi nasara ba – NAHCON

-

Hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON ta ce kasar Saudiyya ba ta amsa rokonsu na sake bude damar samun visar aikin hajjin 2025 ba.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ta ce tana mai bai wa mutanen da abin ya shafa hakuri. Hukumar ta ce duk wanda bai samu visar ba ya tuna cewa hajji kiran Allah ne, ta ce tana shawartar nan gaba mahajjata su rika biyan kudi a kan kari domin guje wa fadawa irin wannan yanayi.

Google search engine

Fatima Sanda Usara wadda ta fitar da sanarwar ta ce hukumar NAHCON ta roki Saudiyya da ta tsawaita wa‘adin rufe bayar da visar a 29/04/2025 kuma Saudiyyar ta bude har zuwa ranar 19/05/2025 da ta rufe kuma ba ta sake budewa ba duk da rokon da NAHCON ta yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin tabbatar da inshorar lafiya a dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnatin Nijeriya

Shugaba Bola Tinubu ya umarci sakataren gwamnatin tarayya da ya fitar da takardar umarni ga dukkan ma’aikatu da hukumomi domin tabbatar da inshorar lafiya bisa...

Zan iya kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga cikin watanni biyu muddin na samu iko da hukumomin tsaro – Gwamnan Zamfara

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa matsalar ayyukan ’yan bindiga da ke addabar jihar za ta zama tarihi muddin ya samu damar bayar da...

Mafi Shahara